kannywood:- Jarumi ya rasa yar uwar sa safiyar ranar sallah
Sanannen jarumi kuma mai shiryawa da bada umarnin fim a masana'antar Kannywood Isah Abubakar Alolo wanda aka fi sani da Sheikh Isa Alolo ya rasa yar uwar shi yayin bikin babban sallah. Jarumin ya sanar da mutuwar yayar sa Binta Abubakar Isah a shafin sa na Instagram. Ta rasu safiyar ranar 21 ga watan agusta wanda tayi daidai da ranar babban sallah. Ya rubuta "Innalillahi wa inna ilaihirraji'un. Allah yayi wa yaya ta rasuwa yau da safe, BINTA ABUBAKAR ISAH ALLAH ya gafarta miki BINTA Allah yasa mutuwa hutu ce A gareki, Allah yasa bakin wahalar ki kenan, Allah yasa Aljanna ce makomar ki..." jim bayan sanar da lamarin sauran abokan sana'ar shi na Kannywood suke ta taya shi ta'aziya tare da jajanta masa inda suka wallafa hotunan marigayiyar a shafukan su na kafafen sada zumunta tare da yi mata addu'a.
Created at
Back to posts
This post has no comments - be the first one!