Old school Easter eggs.
K N T | Keffians News Teller
Babban shafin keffin Magaji dan yamusa wanda yake watsa labarai ta ko ina asassan duniya baki daya

sanarwa


Muna sanar daku cewa Mun kulle wannan shafi, sam ba za mu sake yin Posting a cikinsa ba, sakamakon bude sabon shafin da mukayi mai zaman kansa, sai ku ziyarci shafin akan wannan adireshin www.keffiansloaded.cf dukkan wasu Posts namu yanzu acan zamu runga yi

Notice

we are proudly to inform you that we have upgrade our wepsite , In short this site is bind, abort and close join us in our new wepsite www.keffiansloaded.cf to get our Updates

[littatafan hausa] Bakin artabu cigaban jaruma yazila part 3C

littatafan hausa
A CAN KOFAR BIRNIN MISRA KUWA, Lokacin da gari ya waye sai suka sake yin gagarumin shirin yaki suka fito filin daga. Da fitowarsu suka cika da mamakin domin gani suka yi babu kowa kuma babu komai a sansanin abokan gabar domin sun kwashe komai sun kara gaba. Al'amarin daya dugunzuma hankalin sarki Raihan, Yazila da sauran jama'arsu kenan musamman ma Humaira wacce taci gaba da kuka domin tana ganin cewa shi kenan har abada baza ta sake ganin 'yartaba Dabira. Nan take sarki raihan ya zauna da 'yan majalissarsa suka shiga taro na gaggawa don yanke hukuncin daya kamata akan bacewar abokan gaba. Sai da aka shafe kusan rabin sa'a ana ta kace-nake kowa na fadin shawararsa sannan aka yanke hukuncin abi sawun abokan gaba ataresu ahanya tun gabanninsu isa birninsu domin gara AYITA-TA-KARE yazamana cewa wannan shine yakin karshe daza a yi a tsakanin garuruwan biyu koda za a kwana ana yin BAKIN ARTABU". Nan take kuwa sarki raihan, jaruma Yazila da sauran zakwakwuran mayakan na birnin misra suka sukwani da wakansu suka nausa izuwa cikin daji da gudu domin su cimma abokan gaba. AL-AMARIN su sarki Daksur kuwa tun a daren jiya labari yazo musu cewa ai sarki Uhaisu ya shiga har birnin misra ya kai kansa bisa kamuwa da son Jaruma yazila amma an kamashi an tsare shi a kurkuku, a karshe ya gudu daga kurkukun ya kuma sace gimbiya Yazila ya tafi da ita". Koda jin wannan batu sai farin ciki ya lullube su sarki Daksur domin sun fashimci cewar sarki Uhaisu bai karbi musulunci ba, kuma gashi ya sace Yazila ya kara karfin gabarsa da su sarki Raihan don haka har yanzu shi babban makiyi ne nasu sarki Raihan dole ne ya ci gaba da yin yaki dasu. Batare da bata wani lokaci ba su sarki Daksur suka hada nasu-inasu suka bar sansanin yakin suka durfafi birnin. Sarki Uhaisu domin suje su tayashi murnar bikin aurensa da jaruma yazila. Tabbas sun san cewa ma sai sun riga sarki sarki Uhaisu zuwa birninsa tunda shi a kasa yake ba akan doki ba don haka sai sun zaman jiransa. *** *** *** A CAN cikin daji kuwa sai da sarki Uhaisu da Dabira suka shafe sa'a bakwai suna tafiya sannan sai dabira ta ja ta tsaya cikin mamaki Uhaisu ya juyo ya dubeta yace. "Lafiya kika tsaya kokuwa kin gaji ne?" Dabira ta gyada kai tace, "Lokacin yin ibadata ne yayi" koda jin haka sai Uhaisu ya cika da tsananin mamaki bisa ganin yadda dabira bata wasa da addininta da kuma yadda tayi imani da Ubangijinta dari bisa Dari. Nan take dabira ta sami wuri mai kyau ta tayar da sallah Uhaisu ya koma gefe daya ya zuba mata idanu yana kallon yadda take yin ibadar tata. Abin da ya daure masa kai shine, ganin yadda yanayin ibadar tata yazo irin daya a ko yaushe acikin nutsuwa. Sarki Uhaisu bai daina kallon dabira ba yana sha'awar addininta har ta idar da sallar tayi addu'a ta shafa a dai-dai wannan lokaci ne hadari ya gangamo aka fara walkiya da tsawa. Al'amarin daya razana sarki Uhaisu ke nan ya dubi dabira cikin alamun damuwa yace, "Ya ke abar kaunata, yanzu idan mukace zamu tsaya mu fakewa wannan ruwa mutanenku zasu iya riskemu anan su tarwatsa dukkan shirina koda jin haka sai dabira tayi murmushi tace, "kada kadamu zan roki Ubangijina daya ki sauko da wannan ruwa har sai mun yi nisa sosai mun kusa isa birninka". Cikin alamun rashin yarda da kallon raini ya dubi Dabira yace, "Kada ki raina mini hankali mana, yanzu kina nufin zaki iya rokon Ubangijinki bukata a yanzu take kuma ya biya miki ita?" Dabira tace, "Ai ubangijina yafi gaban haka". Nan take dabira daga kanta da hannayenta sama ta kama addu'o'I. Ai kuwa tana sauke hannayenta sai hadarin ya fara dushashewa kuma nan take aka daina tsawa da walkiya da ake yi. Al'amarin da yai matukar girgiza sarki Uhaisu kenan ya kamu da tsananin mamaki fiye da ko yaushe. Take yaji kaunar addinin musulunci ta darsu a cikin zuciyarsa. Ita kanta dabira sai da ta fashinci cewar Uhaisu yaji wani abu a cikin ransa domin gaba daya jikinsa yai sanyi tamkar bashi da laka. Tafiya ma kasa yiyayi sai data yafitoshi da hannu sannan ya bita a baya suka sake nausawa a cikin daji. Hakika allah shine maiyin yadda yaso. Lokacin da Dabira ta roki allah akan ya tsaida wannan ruwan sama dake shirin saukowa sai ya amsa addu'arta kuma ya nuna ikonsa ya tsayar da ruwan a dai-dai inda suke, amma a sauran wurare a nashiyar gaba daya sai aka tsuge da ruwa kamar da bakin kwarya. Haka dai sarki uhaisu da da bira suka ci gaba da tafiya. Duk sa'adda dabira taji yunwa sai ta cije ta fadawa Uhaisu irin kalar tsuntsun da take sha'awar ci. Dole sai yaje ya farauto irin wannan tsuntsu ya kawo mata kuma shi zai yanka tsuntsun ya fige shi ya gasa mata ya bata taci. Komai kankantar aiki baza ta yishi da kantaba sai dai ta umarceshi dayi, kuma bai taba nuna gajiyawarsa ba. A cikin wannan tafiya tasu ne Uhaisu yayi ta ganin abubuwan al'ajabi atare da dabira wadanda suka shallake tunaninsa domin sau uku suna yin arba da mugayen bakaken aljanu amma da zarar dabira ta fara ambatar sunan ubangijin musulunci sai yaga aljanun sun kama da wuta sun kone kurmus ko kuma suyi sauri su bace. Haka dai suka ci gaba da tafiya har ya zamana cewa suna hango kofar birnin sarki Uhaisu, yazamana cewa ta zarar dake tsakaninsu bata wuce zira'I a shirin ba. Kwatsam! Ba zato ba tsammani sai dabira taga sarki Uhaisu ya yi turjiya ya tsaya cak. A wannan lokaci suna iya hango su sarki daksur tsaitsaye a bakin kofar birnin bisa da wakai cikin matukar farinciki suna daga tutoci alamar cewa suna shirin tarbarsa. Cikin tsananin mamaki dabira ta dubi sarki Uhaisu tace, "Yaya naga ka tsaya, mai makon ka karasa da sauri tun da ga sauran 'yan uwanka can sarakai abokan gabata suna sauraron isowarka domin su tayaka murnar zuwa dani?" Koda jiin wannan tambaya sai sarki Uhaisu ya kawo gwauron numfashi ya ajiye sannan ya dubeta a lokacin da kwalla ta cika masa idanu yace, "Ya ke masoyiyata kiyi sani cewa ba komai ne yasa kika ga na turjeba anan ba face na sauya ra'ayina ne bisa abinda da nake shirin zartarwa akanki. Ba komai ne dalili ba face ganin tsantsar alkawari irin naku na ma'abota addinin musulunci saboda kafin mu fara wannan tafiya sai da kika rantse da girman ubangijinki cewar bazaki yi yunkurin cutar dani ba kuma bazaki gudu ba, gashi kin cika alkawarinki tunda mun iso har birnina baki saba ba. Abu na biyu har a cikin zuciyata naji na gamsu kuma nayi imani cewar babu abin bautawa da gaskiya face ubangijin musulunci, tunda agaban idanuna kin roki ubangijin musulunci a kalla sau hudu bisa bukatarki kuma ya biya miki ita nan take. Ubangijin musulunci ya karemu daga sharrin mugayen bakaken aljanu guda uku wadanda ni kaina ban isa na karemu ba da karfin sihirina ko na damtsena. Tabbas babu abin da yafi cancanta a bautawa sama da ubangijin musulunci. Inaso yanzu ki shigar dani izuwa cikin wannan addini naku mai daraja. " Koda sarki Uhaisu yazo nan azancensa sai hawayen farin ciki yazubowa Dabira, ta dubi sarki uhaisu cikin tsananin murna tace, "Hakika ka sami babban rabo. Ya kai wannan sarki ma'abocin karamci da jin kai tunda har ka karbi addinina to yanzu zan sanar da kai wani babban sirri wanda na boye maka. BASH I TKRW 08105808371
Share Button Back to posts
This post has no comments - be the first one!

Loading...
                 Loading...                  

Rate this