[littatafan Hausa] Bakin Artabu part 3B cigaban jaruma yazila
BAKIN ARTABU
Littafi na uku 3
Na Abdul'aziz sani madakin gini
Typing:- bashir tokarawa
Post:- Shuraih Usman
@shuraih 99%
Part B
Sarki uhaisu yaci gaba da duru-duru kawai sai ya
falfala da gudu kuda dakaru suka ga yana gudau sai
suka bishi sarki uhaisu yana cikin gudu a gidan
sarauta kawai sai ya hango wani mumbari mai tsayi
sai yai sauri ya ya goya dabira a bayansa ya daka
tsalle ya hau kansa munbarin yana hawa ya kara daka
wani tsallen sai gashi ya haure katan gar gidan
sarauta koda masu gadin kofar birnin suka ganshi
goye da jaruma dabira sai suka bishi aka kasa tsere.
Al'amarin sarki uhaisu kuwa lokacin da ya kama
azababben gudu goye da jaruma dabira a bayansa
wadannan dakaru masu gadin kofar na biye dashi
amma sai suka kasa cimmasa domin tazarar da
yabasu bakadan bace.
Koda suka ga baza su iya cimmasa ba sai suka fara
zaro kibiyoyi suna danawa suna kai harbi.
Sai da suka shafe rabin sa'a suna gudu su basu
cimmasa ba shi kuma bai bace musuba. Ana cikin
hakane wani acikin dakarunnan mai shegen naci
yasamu nasarar hatbin sarki uhaisu akafarsa ta hagu
Koda kibiyar ta sokeshi a sangalelen kafarsa ta faso
nama ta fito jini yai tsartuwa sai sarki uhaisu ya
tsandara ihu sakamakon tsananin zafi da zugi da yaji
amma saboda tsananin juriya da jarumtaka bai fadi
ba kuma bai tsaya ya zare kibiyar ba, yacibgaba da
gudu a hakan, mai makon ma ya sare sai ya sami
karin kuzari da karfin gudun nasa ya kara tsananin
tamkar iska ce ke kara shi gaba. Nan da nan cikin
kankanin lokaci ya sake baiwa dakarun tazara mai
yawan gaske ya bace musu bat da gani.
Haka dai sarki uhaisu yaci gaba da falfala gudu har
sai daya bar cikin daji ya nausa ya sake yin tafiya mai
nisa ta tsawon kimanin sa'a uku a sannan ne jiri ya
fara dibarsa saka makon. Jinin dake zuba a kafarsa.
Kawai sai ji yayi ya yanke jiki ya fadi kasa da ruf da
ciki a matukar galabaice a sannanne ya samu ya
kwance dabira daga bayansa ya shimfideta a gefe
sannan ya dubi kibiyar dake nutse a cikin kafarsa,
gajini na zuba kawai sai takaici yarufe shi sakamakon
tunowa da cewa soyayyace ta janyo masa wannan
kaskancin a matsayinsa na sarki mai cikakken iko
kuma sadaukin jarumi mai dakawa maza gumba
ahannu, wanda bai taba guduwa ba a filin daga balle
ya ja dabaya.
Nan da nan sarki Uhaisu ya mike tsaye da kyar yaje
ya samo kiraren wuta da kyastu ya hada wuta sannan
ya sanya wuka a cikin wutar domin ta gasu tayi jajir.
Sai da wukar ta gasu ainun sannan yasa hannu ya
zate wannan kibiya daga cikin kafatsa farat daya cikin
zafin nama aikuwa sai ya sake tsandara uban ihu
sakamakon tsananin zafi da zugi.
Cikin dauriya ya dauko wannan wuka ya dodanata
akan ramin raunin da kibiyar tayi masa ya soye, ya ci
gaba da ihu har ya gama soye raunin duka. A sannan
ne kuma ya sake mikewa tsaye ya tafi neman ganyen
wata bishiya.
Cikin sa'a ya samo ganyen da wuri ya dauko ya dawo
inda dabira ke kwance ya zauna ya dandaka wannan
ganye ya shafashi akan raunin kafar tasa don kada
kunar ta tashi ta zama ciwon kuna.
Faruwar hakan keda wuya sai Dabira ta farka. Koda ta
bude idanunta ta tsinci kanta a cikin daji kuma taga
sarki Uhaisu zaune agabanta yana yimata murmushi
sai ta doki kirjinsa da kafarta ya hantsila baya ta
falfala da azababben gudu. Aikuwa sai yamike
zumbur! Ya bita da gudu. Kafin cikar dakika biyar ya
kure mata gudu ya sha gabanta. Nan fa suka kaure da
fada ta rinka kai masa bugu da naushi da dukkan
karfinta shi kuwa ya rinka kare dukkan hare-haren
nata ba tare da ya maida mata martaniba.
Koda ya ga tana neman ta cutar da shi sai ya nuna
mata tsagwaron karfin damtse gami da fifikon
kwarewa ya sureta sama ya damfarata da kasa ya
danneta da ruf da ciki ya murde hannayenta duka
biyu a bayanta. Ya dauresu ta mau da yankin nan
wanda ya goyata da shi abaya sannan ya tasheta
zaune shima ya zauna suka fuskanci juna tana
harararsa shi kuma yana yimata murmushi. "
Cikin murya mai taushi sarki uhaisu ya dubi dabira
yace, "Ya ke ma abociyar kyawu kiyi sani, cewa ban
kawoki nan domin na cutar dakeba sai dan kamuwa
da tsananin kaunarki da zuciyata tayi idan kika yimin
alkawarin bazai sake yunkurin guduwaba kuma
bazaki cutar daniba zankwance ki yanzunnan.
Ina son ki bani soyayya ta gaskiya kamar yadda
zuciyata ta kamu da tsaninin sonki domin na kaiki
birnina ki zama sarauniyata kuma abokiyar rayuwata
ta har abada"
Koda sarki Uhaisu yazo nan azancensa sai dabira ta
tofa masa yawu a fuskarsa tace, "Har abada babu
soyayya da amana tsakanin ruwa da wuta.
Ka sani cewa ni musulmace, kai kuma kafirine don
haka mun zama hannun riga babu ta inda zamu iya
zama tare.
Na rantse da girman Ubangijinaa bazan taba baka
irin soyayyar da kake bukataba.
Ina mai shawartar ka da ka kwanceni kuma ka sakeni
na koma izuwa ga birnina kuma ka cire soyayyata
daga cikin zuciyarka domin zai fiye maka alheri. "
Sa'adda dabira tazo nan a zancenta sai sarki uhaisu
ya kamu da tsananin bakin ciki gami da takaici har ya
daga hannu zai mangareta sai ya kasa ya kura mata
idanu kawai a lokacinda kwallar ta kaici tazo masa ya
tuna cewa tunda uwarsa ta haifeshi yazo duniya ba a
aba tofa masa yawu a fuskaba sai yau. Shin dama
haka soyayya take, kana son mutum amma kuma shi
ya tsaneka?". Sarki uhaisu ya tambayi kansa a cikin
zuciyarsa.
Lokacin da Dabira taga sarki uhaisu ya kura mata
idanu har kwallar takaici ta cika masa idanuwa sai
tausayinsa ya kamata taji kamar ta gaya masa gaskiya
cewar ba ita bace gimbiya yazila wacce ya kamu da
tsananin sonta amma sai wata zuciyar ta haneta sarki
Uhaisu ya mike tsaye ya koma gefe daya ya tsaya
yana tunanin abin da zai fishsheshi.
Kawai sai yaji dabira tace, "Nifa kishirwa nakeji".
Koda jin wannan batu sai hankalinsa ya dugunzuma
domin ya fashimci cewar babu ruwa a kusa kuma
gashi dare ne sosai ga tsananin duhu a cikin dajin
amma kuma sai yaji cewar ba zai iya barinta da
kishirwa ba dole ne ya je ya samo mata ruwan.
Kawai sai ya taho gareta da nufin ya kamata ya goyata
a bayansa su tafi neman ruwan amma sai ta dakatar
dashi da hannayenta tana mai daka masa tsawa tace,
"Kai mufa a addininmu haramunne na mijin da ba
muharraminka ba ya taba jikinka.
Daga yau kada ka sake kusantata, kawai ka kwance
mini hannayena na taka da kafafuna mu tafi neman
ruwan tunda yanzu ko ka kyaleni kayi bazan iya
komawa birninmu ba domin kaina ya juye ban ma
gane a ina nake ba yanzu kuma ga tsananin duhu a
wannan daji zan iya fadawa cikin wani wurin dazan
iya cutuwa ko na hallaka".
Sarki Uhaisu ya dubi dabira cikin alamun rashin
yarda yace, "Menene tabbacin cewar idan na
kwanceki bazaki cutar dani ba kuma bazaki gudu ba?"
Dabira tayi dan guntun murmushi a gareshi tace, "Na
rantse da girman ubangijina bazan guduba kuma
bazanyi yunkurin cutar dakaiba bisa sharadi guda
sharadin kuma shine ba zamu rinka kwanciya a waje
daya ba daga nan har muje birninka kuma zaka
kyaleni na rinka yin ibadata".
Koda jin haka sai sarki Uhaisu yayi murmushi yace,
"Ai wannan mai saukine, na yi alkawari duk zan yi
kamar yadda kika bukata".
Koda gama fadin hakan sai sarki Uhaisu ya kwance
hannayen Dabira daga daurin da yayi mata ya dubeta
ya ce, "Na san cewa kuna kiyaye darajar Ubangijinku
da girmansa don haka na yi imanin baza ku rantse da
shi ba kuma ku saba alkawarin, shi yasa na amince
na kwanceki yanzu sai kizo mu tafi neman ruwa".
Koda gama fadin hakan sai ya dauki ice daya daga
cikin kiraren nan daya kunna wuta sannan ya
nannadeshi da yankin nan na damararsa ya cinna
wuta ya rikeshi a matsayin fitila dazata. Haska musu
hanya ka wai sai ya nausa daji take dabira ta bishi a
baya da sauri, sai da suka shafe kusan rabin sa'a
suna neman ruwa basu samu ba sannan suka riski
wata korama wacce ruwanta ke zubowa ta kan saman
wadansu duwatsu. Ruwane garai-garai har wani irin
kamshi yake mai dadi.
Cikin matukar farinciki Dabira da Uhaisu suka ruga
izuwa bakin kooramar suka tsugunna suka sha
sannan suka dawo gefe suka zauna.
A sannan ne wata irin iska mai tsananin sanyi ta fara
kadawa wacce tasa jikinsu ya kama karkarwa kawai
sai dabira ta dubi sarki Uhaisu a fusace tace, "Ya za a
yi ka baroni da gidanmu inda na saba kwanciya a
cikin daki kuma akan shimfida mai taushi kakawoni
nan cikin daji inda sanyi ma zai iya lahantani?
Hakika ka zalunceni kuma ka cutar da ni. Haka ake yin
SOYaYYA ka cutar da masoyinka?"
Koda jin wannan batu sai hankalin sarki Uhaisu ya
dugunzuma ainun ya dubi dabira cikin alamun
tsananin da muwa yace, "KI gafarceni ya masoyiyata
yanzun nan zan magance miki wannan sanyi da ya
dameki".
Yana gama fadin hakan ya mike tsaye yaje ya kama
saran bishiya sai da ya karyo rassa dogaye da masu
kauri da yawa sannan yazo ya shiga aikin gina daki.
Har ya kammala ginin dakin da itatuwa ya lullubeshi
da ganye Dabira na zaune tana kallonsa kawai tana
mamaki.
A zuciyarta tana cewa, "yanzu kawai saboda ya kamu
da soyayya yake ta wahala yake ta wahalar da kansa
haka? Lallai kuwa ashe gaskiyar masu iya magana da
suka ce "SOYAYYA dafice wacce in ta shiga jikin
mutum bata fita har ajali"
Bayan sarki Uhaisu ya gama gina dakin ice har da
kofarsa ta shiga sai kuma yaje ya nemo ganyaye
masu fadi da taushi yazo ya yiwa Dabira shinfida
dasu a cikin dakin sannan yace ta shiga cikin dakin ta
kwanta shi zai tsaya. A waje yayi gadin ta don kada
wata dabbar daji tazo ta cutar da ita".
Ba tare da gardamar komai ba kuwa dabira ta shiga
cikin dakin ta turo kofa ta rufe tayi kwanciyarta ba
tare da ta sake jin wani sanyi ba. A sannan ne fa taji
tausayin sarki Uhaisu ya kamata domin ta san cewa
ba karamar wuya zai shaba idan ya kwana a filin allah
cikin wannan tsananin sanyin.
Saukinsa daya ya hura wuta wacce zai rinka jin dumi,
kuma koda wutar barci dai bazai yiwuba a wajensa
kuma wannan sanyin zai iya cutar dashi.dabira taji
kamar ta tashi ta bude masa dakin tace ya shigo
amma data tuna cewa abune mai hadarin gaske a
addinance ta kwanta da. Wani da namiji a cikin dakin
sai ta fasa.
A suba nayi Dabira ta farka daga barci ta bude dakin
ta fito waje domin tayi alwala. Tana fitowa taga sarki
Uhaisu zaune a gaban wuta yana jin dumi amma
jikinsa na ta karkarwar dari kuma idanunsa sunyi
jawur sakamakon rashin samun barci.
Nan take taji tausayinsa amma sai ta murtuke fuska
ta kau da kai ga barin kallonsa taje bakin wannan
korama ta tsugunna tayi alwala sannan ta mike tsaye
ta fuskanci alkibla ta tayar da sallah.
Bayan ta idar da sallar ne ta shiga yin addu'o'I bata
gushe ba tana yin addu'o'in har sai da alfijir ya keto
gari ya fara haske sannan ta shafa addu'ar ta waigo ta
dubi sarki Uhaisu tace, "Menene abin yi yanzu?
Zaka nemo mini abincin kalaci ne ko kuma zamu ci
gaba da tafiya ne?"
Uhaisu ya dubeta cikin alamun damuwa yace, "Ki
gafarceni ya masoyiyata bai kamata mu tsaya yin
kalaciba anan domin ina zargin cewa mutanenku sun
biyo sawummu, gwara mu kara gaba muyi nisa
tukunna sai mu yada zango na nemo mana abincin
kalaci".
Ba tare da gardamar komaiba Dabira tace, "Na
amince da hakan".
Nan take suka hada nasu-inasu suka bar wannan daji
suka kara gaba.
Babban kuskuren da sarki Uhaisu yayi shine da bai
rushe wannan daki daya gina ba kuma bai batar da
ragowar wutar daya kunna ba domin sun zamo
alama ta cewar suna cikin wannan daji shida gimbiya
Dabira.
Wannan shine abinda ya faru tsakanin sarki Uhaisu
da gimbiya Dabira bayan ya satota daga gidan
sarutar sarki Raihan a matsayin masoyiyarsa Jaruma
YAZILA wacce ya kamu da tsananin kaunarta kuma
yake son ta zamo abokiyar rayuwarsa ta har abada.
BASH I TKRW
08105808371
Created at
Back to posts
This post has no comments - be the first one!