Za A Hukunta Masu Sayar Da Jakunkunan Makaranta Na UNICEF
Gwamnatin Jihar Nasarawa ta yi barazanar hukunta duk wanda aka kama yana sayar da jakunkunan makaranta da ke dauke da rubutun Asusun gidauniyar tallafawa yara ta duniya (UNICEF). Babban sakatare na ofishin shugaban ma’aikatan Jihar Mista Dauda Sabo, ya sanar da hakan a sanarwar da ya fitar a garin Lafia a jiya Alhamis. Sabo, ya bayyana cewar jakankunan makarantar, ya kamata ne a rabawa yara ‘yan makaranta amma ba sayar da su ba. Ya danganta masu sayar da jakunkunan a matsayin masu laifi, kuma duk wanda gwamantin Jihar ta kama za ta hukunta shi. Sakataren ya yi kira ga iyaye da su kawo rahoton duk wanda suka gani yana sayar da jakunkunan. A karshe, Sabo ya umurci jami’an tsaro da su cafko masu sayar da jakunkunan don a hukunta su. Hausa Kano News 9JA News BBC Hausa Video Leadership
Created at
Back to posts
This post has no comments - be the first one!